Tinubu ya bukaci ‘Yan Nijeriya su sauya Halayen su

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci ƴan Najeriya da su sauya halayen su a kan kasar tasu.

Shugaban dai na magana ne yayin da ya karɓi baƙuncin tawaga daga majalisar dokokin ƙasar waɗanda suka kai masa ziyarar barka da sallah.

Tinubu ya ce “lokaci ya yi da ƴan Najeriya za su sauya hali da tunaninsu ga Najeriya domin ciyar da ƙasar gaba”.

“Yan ƙasa da ke yawon neman wayar lantarki domin su cire da tuge titin dogo da dai sauran ayyukan ɓaagari, E, na amince akwai talauci, akwai wahalhalu. Amma ba mu kaɗai ne mutanen da muke shan wahala ba. Dole ne mu tunkari kalubalen da ke gabanmu.” In ji Tinubu.

Ya ƙara da cewa “akwai bukatar wasu ƴan ƙasar su sauya tunaninsu su kuma zama masu taimakawa wajen warware ƙalubalen da tattalin arziƙin ƙasar ke fuskanta. Saboda haka akwai buƙatar daina fasaƙwauri da cin dunduniyar tattalin arziƙin.”

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 37 minutes 56 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 19 minutes 21 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com