Gwamnatin Kano ta zargi Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar.

Gwamnatin jihar Kano ta zargi rundunar ‘yan Sandan jihar da daukar bangaranci a rikincin Masarautar dake faruwa a jihar.

Daraktan yada labaran Gwamnan jihar Sunusi Bature Dawakin Tofa ne ya bayyana hakan ta cikin wata hira da tashar Talabijin ta Channels a cikin shirin Politics Today na ranar Juma’a.

Idan za’a iya tunawa tun bayan da majalisar jihar kano ta yiwa dokar masarautar jihar gyaran fuska, gwamnan jihar ya umarci kwamishinan ‘yan sandan daya fidda tsohon sarki Aminu Ado bayero daga fadar sarkin ta gidan Rumfa.

Sai dai rundunar ‘yan sandan bisa jagoranci CP Usaini Gumel tayi fatali da umarnin gwamnan inda tace umarnin kotu yafi dacewa ta bi.

Ta cikin ganawar Sunusi Bature ya bayyana cewa hukuncin Kotun tarayya su ya bawa nasara domin kuwa kotun bata rushe dokar data sauke tsoffin sarakunan jihar guda biyar ba.

Daga bisani Dawakin Tofa ya bayyana muhimmancin dawo da martabar sarautar kano da ya zargi tsohuwar Gwamnatin Ganduje da kassarawa.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 40 minutes 11 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 21 minutes 36 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com