Home DUNIYA NCDC ta ce bata da wadatacciyar Allurar Rigakafin Kwalara

NCDC ta ce bata da wadatacciyar Allurar Rigakafin Kwalara

Hukumar dake dakile yaduwar cuttukka ta Nijeriya NCDC tace bata da wadatacciyar Allurar ragakafin cutar kwalara.

Daraktan hukumar Dr. Jide Idris ne ya bayyana hakan, inda yace kasar ta bayar da sallahun allurar ga hukumomin dake da alhakin sayar da ita a duniya da masu bayar da tallafinta, duk da cewa bai bayyana ranar da allurar zata iso ba.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da rahotannin ke bayyana yadda mutane 40 suka mutu sakamakon kamuwa da cutar ta kwalara a kasar nan.

Dr. Jide ya bukaci al’ummar kasar nan da su yi amfani da allurer rigakafin da wasu matakan kariya daga kamuwa da cutar ta kwalara.

Cutar kwalara dai na guda cikin cututtukan da ake daukar su ta hanyar shan ruwa ko abinci maras tsafta, wanda takan kai ga hallaka mutun bayan kamuwa da ita.

Bincike dai ya nuna cewa a cikin shekaru hudu da suka gabata cutar ta hallaka mutane 4,364 yayin da aka zargi mutane 139,730 da suka kamu da cutar a kasar nan.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp