Gwamnatin Jihar Sokoto ta Musanta yunkurin cire Sarkin Musulmi

Gwamnatin jihar Sokoto ta musanta zargin cire mai alfarma sakin musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III,

Wannan na cikin wata sanar wada mai Magana da yawun Gwamnan jihar Abubakar Bawa ya fita aka raba ta ga manema labarai, sanarwar kuma bukaci Mataimakin Shugaban ƙasa Kashim Shettima ya rika bincike kafin yin sharhi kan duk Wani Labari da ya gani a kafofin sadarwa na zamani.

“Munyi zaton mataimakin shugaban kasa ya tuntubi Gwamnan Jihar sokoto kafin ya fito fili yayi magana akan Batun Tsige Sarkin Musulmi.

“gaskiyar magana ita ce, ba’a taba yunkurin tsige Sarkin ba, haka kuma ba mu aika masa da wata barazana ba dangane da hakan ba a cewar Sanarwar”

Sanarwar ta kara da cewa, Sarkin Musulmi na cin moriyar duk wani ikon da yake da shi, ba mu taba tauye masa wani ‘yanci ko hakkinsa ba”

Haka Gwamnati da al’ummar Jihar Sokoto na girmama Majalisar Sarkin Musulmi kuma zasu yi duk mai yiwuwa don kare martabar wannan Masarautar”.

“Daga bisani gwamnati na tabbatarwa ‘yan Nijeriya cewa, za ta cigaba da kare Majalisar Sarkin Musulmi da mutuncinta a kowane lokaci”

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 5 minutes 42 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 47 minutes 7 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com