Home DUNIYA Maitamakin shugaban hukumar Kwastom ya mutu a zauren majalisar wakilai

Maitamakin shugaban hukumar Kwastom ya mutu a zauren majalisar wakilai

Rahoyanin daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa mataimakin Shugaban hukumar hana fasa kwari ta Kasa dake lura da harkokin kudi da gudanarwa Essien Etop Andrew ya yanke jiki ya fadi a gaban zauren Majalisar wakilan Nijeriya.

A yayin da yake amsa tambayoyin a gaban ‘yan majalisar wakilan Andrew ya sarke, wannan ne ya sanya shi faduwa kasa magashiyyan.

Jaridar Solacebase ta ruwaito cewa masu bayar da agajin gaggawa na majalisar sun garzaya da shi asibiti amma abin yaci tura ya kai ga  mutuwar sa.

Ta cikin wata sanarwa da mai Magana da yawun majalisar wakilan Akin Rotimi, ya fitar ta ce majalisar zata bayar da gudunmawar don ganin an fahimci lamari da abinda ke kewaye da shi ga dukkanin masu ruwa da tsaki.

Haka kuma ta ce kakakin majalisar Tajuddeen Abbas, ya mika sakon ta’aziyyar sa ga iyalai da hukumar ta NCS, yace majalisar ta damu matuka da mutuwar jami’an

Bamidele Salam wanda shike jagorantar Kwamitin dake bincike ya ce kwamitin ya dage zaman zuwa mako guda domin girmama marigayin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp