Home DUNIYA Maitamakin shugaban hukumar Kwastom ya mutu a zauren majalisar wakilai

Maitamakin shugaban hukumar Kwastom ya mutu a zauren majalisar wakilai

Rahoyanin daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa mataimakin Shugaban hukumar hana fasa kwari ta Kasa dake lura da harkokin kudi da gudanarwa Essien Etop Andrew ya yanke jiki ya fadi a gaban zauren Majalisar wakilan Nijeriya.

A yayin da yake amsa tambayoyin a gaban ‘yan majalisar wakilan Andrew ya sarke, wannan ne ya sanya shi faduwa kasa magashiyyan.

Jaridar Solacebase ta ruwaito cewa masu bayar da agajin gaggawa na majalisar sun garzaya da shi asibiti amma abin yaci tura ya kai ga  mutuwar sa.

Ta cikin wata sanarwa da mai Magana da yawun majalisar wakilan Akin Rotimi, ya fitar ta ce majalisar zata bayar da gudunmawar don ganin an fahimci lamari da abinda ke kewaye da shi ga dukkanin masu ruwa da tsaki.

Haka kuma ta ce kakakin majalisar Tajuddeen Abbas, ya mika sakon ta’aziyyar sa ga iyalai da hukumar ta NCS, yace majalisar ta damu matuka da mutuwar jami’an

Bamidele Salam wanda shike jagorantar Kwamitin dake bincike ya ce kwamitin ya dage zaman zuwa mako guda domin girmama marigayin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp