Home General Ricikin Manoma da makiyaya ya yi sanadin mutuwar mutum 2 a jihar...

Ricikin Manoma da makiyaya ya yi sanadin mutuwar mutum 2 a jihar Jigawa

Rundunar ‘yan sandan jihar jigawa ta tabbatar da mutuwar mutum 2 tare da kone gidaje 3 bisa wata arangama tsakanin manoma da makiyaya a karamar hukumar Birnin Kudu dake jihar.

kakaikin rundunar ‘yan sandna jihar DSP Lawan Shiisu Adam ne ya tabbatar da hakan inda yace jami’an ‘yan sandan hadin gwiwa da jami’an tsaron Civil defence da kuma dakarun sa kai na bijilanti. sun sami nasarar kwantar da rikicin tare da kama mutum 5 da kuma shanu guda biyar da aka yasar.

Shaidun gani da ido sun tabbatar da cewa makiyayan da suka fito daga jihar Katsina, sun tasamma yankin da tarin garken shanu, inda suka fara lalata amfanin gonar da manoma suka shuka, wannan ne ya sanya manoman daukar matakin kare gonakinsu da rayukansu.

yace arangamar ta haddasa mutuwar mutum 2 daga ko wanne bangare tare da kone gidaje 3 mallakin alúmmar garin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp