Home DUNIYA Tinubu ya taya Starmer murnar zama sabon Firaministan Birtaniya

Tinubu ya taya Starmer murnar zama sabon Firaministan Birtaniya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya taya sabon firaministan Birtaniya Sir Keir Starmer, murnar kama aiki, bayan nasarar da jam’iyyarsa ta yi a zaɓen ƙasar.

Cikin wata sanarwa da kakakin shugaban na Najeriya, Ajuri Ngelale ya fitar, ya ce a matsayin Tinubu na tsohon jigon adawa a Najeriya, ya san yadda sabon firaministan ke da ƙwarin gwiwa kan sabon aikin da ya kama.

”Shekarun da ya kwashe yana jagorantar jam’iyyar hamayya sun ba shi damar sake shiryawa domin sake karɓar iko”, in ji Tinubu.

Shugaban na Najeriya ya ce yadda jam’iyyar ta yi shirin ta kuma sake karɓar mulki bayan shekara 14 ya nuna yadda mista Starmer ke da kyawawan halaye da ɗabi’u na shugabanci.

Shugaba Tinubu ya kuma ce a shirye Najeriya take don yin aiki tare da sabon firaministan don ƙara yauƙaƙa danƙon zumunci da ƙarfafa dimokraɗiyya da kasuwanci da ci gaba tsakanin ƙasashen biyu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp