Ƙudirin da ke neman ƙirƙiro sabuwar jiha a yankin kudu maso gabashin Najeriya ya tsallake karatu na biyu a Majalisar Wakilai.
Ƙudirin yana neman a ƙara jihar Etiti a yankin mai jihohi biyar kuma ‘yanmajalisa Amobi Ogah (LP, Abia), Miriam Onuoha (APC, Imo), Kama Nkemkama (LP, Ebonyi), Chinwe Nnabuife (YPP, Anambra), da kuma Anayo Onwuegbu (LP, Enugu) ne suka gabatar da shi.
Ogah ya ce niyyarsu ita ce kawo ƙarshen abin da aka daɗe ana tattauna a kai na yawan jihohi a yankin nasu. Suna so ne a yanki jihar daga jihohin yankin na Anambra, Imo, Ebonyi, Abia, and Enugu.
Yayin zaman na jiya Alhamis, an amince da ƙudirin ne a mataki na biyu ba tare da wata muhawara ba daga ‘yanmajalisar, inda suka amsa amincewa lokacin da Kakakin Majalisa Tajudeen Abbas ya nemi kaɗa ƙuri’a da baki.
A ranar Laraba ma Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila ya gabatar da ƙudirin neman ƙirƙiro jihar Tiga daga Kano a arewa maso yammacin ƙasar.
PRNigeria hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1190 days 9 hours 30 minutes 54 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 12 minutes 19 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com