Home DUNIYA Kudirin kirkiro sabuwar jihar Etiti a Najeriya ya tsallake karatu na biyu

Kudirin kirkiro sabuwar jihar Etiti a Najeriya ya tsallake karatu na biyu

Ƙudirin da ke neman ƙirƙiro sabuwar jiha a yankin kudu maso gabashin Najeriya ya tsallake karatu na biyu a Majalisar Wakilai.

Ƙudirin yana neman a ƙara jihar Etiti a yankin mai jihohi biyar kuma ‘yanmajalisa Amobi Ogah (LP, Abia), Miriam Onuoha (APC, Imo), Kama Nkemkama (LP, Ebonyi), Chinwe Nnabuife (YPP, Anambra), da kuma Anayo Onwuegbu (LP, Enugu) ne suka gabatar da shi.

Ogah ya ce niyyarsu ita ce kawo ƙarshen abin da aka daɗe ana tattauna a kai na yawan jihohi a yankin nasu. Suna so ne a yanki jihar daga jihohin yankin na Anambra, Imo, Ebonyi, Abia, and Enugu.

Yayin zaman na jiya Alhamis, an amince da ƙudirin ne a mataki na biyu ba tare da wata muhawara ba daga ‘yanmajalisar, inda suka amsa amincewa lokacin da Kakakin Majalisa Tajudeen Abbas ya nemi kaɗa ƙuri’a da baki.

A ranar Laraba ma Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila ya gabatar da ƙudirin neman ƙirƙiro jihar Tiga daga Kano a arewa maso yammacin ƙasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp