Home DUNIYA Gini mai hawa 2 ya hallaka dalibai 16 a jihar Filato

Gini mai hawa 2 ya hallaka dalibai 16 a jihar Filato

Aƙalla ɗalibai 16 ne suka mutu bayan ruftawar ginin mai hawa biyu a wata makaranta a birnin Jos na jihar Filato da ke tsakiyar Najeriya ranar Juma’a da safe.

Rahotonni sun ce ɗalibai masu yawa ne suka jikkata, yayin da ɗaliban da malamai suka maƙale a cikin ginin.

Ginin na makarantar Saint Academy – da ke unguwar Busa-buji a ƙaramar hukumar Jos ta Arewa – ya rufta ne a lokacin da ɗaliban ke ɗaukar darussa.

Iyayen yara sun cika harabar makarantar bayan faruwar lamarin, domin sanin halin da ‘ya’yansu ke ciki, yayin da waɗanda suka ga gawarwakin ‘ya’yansu suka kiɗime.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Najeriya (NEMA) na ci gaba da aikin ceto domin zaƙulo sauran mutanen da ginin ya danne.

Kawo yanzu an gano gawargwaki aƙalla 16, to sai dai har yanzu ba a san adadin mutanen da suka mutu ba.

Akwai dai fiye da ɗalibai 1,000 a makarantar. Kawo yanzu dai ba a san dalilin da ya haddasa ruftawar ginin ba

Iyayen ɗalibai sun garzaya asibitin birnin Jos domin sanin halin da ‘ya’yansu ke ciki.

Likitoci na kira ga al’umma su bayar da gudunmowar jini domin ceto rayukan ɗaliban da aka kai asibitin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp