Rundunar Sojojin Saman Nijeriya ta tarwatsa maboyar ‘yan ta’adda a jihar Kaduna

Rundunar Sojojin saman Nijeriya tace ta sami nasarar tarwatsa maboya ‘yan ta’adda masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, a garin kufam shantu dake karamar hukumar giwa dake jihar kaduna a arewa maso yammacin kasar Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na rundunar Air vice Marshal Edward Gabkwet ya fitar a ranar lahadi.

Sanarwar ta ce daya daga cikin atisayen da rundunar sojin ta kai a ranar 12 ga watan Yuni a maboyar ‘yan ta’adda ta Alhaji layi, wadda suka sami nasarar tarwatsa ta da kuma kometa.

Haka kuma a wani harin makamancin wannan da rundunar ta gudanar ranar 13 ga watan na Yuni kan ‘yan bindigar a cikin dajin malum dake karamar hukumar Igabi, wadda rundunar ta ce ta sami gagarumar nasara.

Jihar kaduna dai na guda cikin jihohin dake arewacin Nijeriya dake fama da matsalolin rashin tsaro da suka addabi al’ummar ta musamman masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa.

PRNigeria hausa

 

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 13 hours 50 minutes 0 second,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 15 hours 31 minutes 25 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com