Home DUNIYA Rundunar Sojojin Saman Nijeriya ta tarwatsa maboyar ‘yan ta’adda a jihar Kaduna

Rundunar Sojojin Saman Nijeriya ta tarwatsa maboyar ‘yan ta’adda a jihar Kaduna

Rundunar Sojojin saman Nijeriya tace ta sami nasarar tarwatsa maboya ‘yan ta’adda masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, a garin kufam shantu dake karamar hukumar giwa dake jihar kaduna a arewa maso yammacin kasar Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na rundunar Air vice Marshal Edward Gabkwet ya fitar a ranar lahadi.

Sanarwar ta ce daya daga cikin atisayen da rundunar sojin ta kai a ranar 12 ga watan Yuni a maboyar ‘yan ta’adda ta Alhaji layi, wadda suka sami nasarar tarwatsa ta da kuma kometa.

Haka kuma a wani harin makamancin wannan da rundunar ta gudanar ranar 13 ga watan na Yuni kan ‘yan bindigar a cikin dajin malum dake karamar hukumar Igabi, wadda rundunar ta ce ta sami gagarumar nasara.

Jihar kaduna dai na guda cikin jihohin dake arewacin Nijeriya dake fama da matsalolin rashin tsaro da suka addabi al’ummar ta musamman masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa.

PRNigeria hausa

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp