Home General Shugaban NNPC ya mayarwa da Dangote Martani

Shugaban NNPC ya mayarwa da Dangote Martani

Shugaban kamfanin NNPC Mele Kyari ya mayar wa attajirin Afirka Aliko Dangote martani bayan zargin cewa wasu mutanen NNPC sun mallaka kamfanin tace mai a ƙasashen ƙetare.

A sanarwar da ya wallafa a shafinsa na X, Mele Kyari ya yi watsi da zargin inda ya ce ba shi da wani kamfani na tace mai a ƙasashen ƙetare.

A wani bidiyo da ke yawo a kafofin sada zumunta, Aliko Dangote ya yi zargin cewa wasu ƴankasuwar mai da mutanen NNPC sun buɗe kamfanin tace mai a Malta.

“Mun san inda ake wannan aikin kuma mun san me suke yi, ba wai ba mu sani ba,” in ji Dangote.

Da yake mayar da martani, Shugaban NNPC ya ce “ba ni da wani kasuwanci ko wanda ake yi da sunana a ko’ina a duniya idan ba wanda nake yi ba gida na aikin gona.”

“Sanna ba ni da masaniya ko akwai ma’aikacin NNPC da yake da matata a Malta ko wani wuri a sassan duniya.”

Shugaban na NNPC ya buƙaci a fallasa waɗanda Dangote yake zargi tare da sanar da jami’an tsaro domin ɗaukar matakin da ya dace da su.

A cikin bidiyon da ke yawo na Dangote, ya yi zargin ana shigo da man da ba ya da inganci a Najeriya, dalilin ya sa wasu ke samun matsaloli a motocinsu, a cewarsa.

Ya ce idan har ana son tabbatar da gaskiyar abin da yake fada – abin da ya kamata a gudanar shi ne gwaji kan man da ake sayarwa a gidajen mai amma ba daga tashar ruwa ba.

“Wani kawai zai shigo da jirgin ruwa ya gabatar da samfuri da takardar bogi sai a sahale masa – nan gaba za mu ci gaba da magana,” in ji Dangote.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp