Home General Zanga – Zanga babu gudu ba ja da baya a Kano –...

Zanga – Zanga babu gudu ba ja da baya a Kano – WAI

Ƙungiyar kare haƙƙin Ɗan Adam, yaƙi da rashin adalci dama bibiya akan shugabanci na gari wato War Against Injustice (WAI), ta ce babu gudu babu ja da bayan akan Zanga-zangar da ta ayyana gudanarwa daga ranar 1 ga watan Agusta zuwa 10 ga wata.
Babban daraktan ƙungiyar Kwamared Umar Ibrahim Umar ne ya sanar da hakan ta cikin wani saƙon murya da jaridar GTR HAUSA ta samu a yammacin talata, inda ya ce matakin ya zama dole domin nunawa mahukunta halin da talaka yake ciki.
A cewar Kwamared Umar “Ina wannan magana ne a matsayin martani dangane da taron manema labaran da wata ƙungiya tayi a jiya wadda ta ce sun janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa, adan haka mu bamu janye ba kuma zamu gudanar a ranakun da muka ayyana.
Ya ƙara da cewa zasu gudanar da zanga-zangar tasu cikin lumana da kwanciyar hankali kuma ba tare da taɓa haƙƙin al’umma ba, ta yadda zasu nunawa duniya halinda talakawan ƙasar ke ciki na yunwa, fatara da kuma talaucin da yayi musu katutu.
A ƙarshe ƙungiyar tayi fatan Al’ummar jihar zasu basu haɗin kai da goyon baya domin ayi lafiya kuma a kammala lafiya.
A jiya ne ƙungiyar Shugabannin Matasan Arewacin Najeriya ta ce ta janye zanga-zangar da ta shirya gudanarwa, a sakamakon yadda ta gano akwai masu ƙoƙorin rikita ƙasar ta hanyar amfani da zanga-zangar tasu.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp