Rushewar gini ta hallaka mutum uku a jihar Lagas

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Legas ta tabbatar da mutuwar mutum uku a lokacin da wani gini ya rufta a rukunin gidajen Arowojobe da ke yankin Maryland a jihar.

Babban sakataren hukumar, Dakta Olufemi Oke-Osanyintolu ne ya bayyana hakan ga Kamfanin dillanci labarai na kasa NAN, inda ya ce lamarin ya faru ne da tsakar daren ranar Alhamis.

Ya ce mutane ukun da suka mutu a lokacin faruwar lamarin duka ma’aikatan gini ne.

“Bayan samun labarin faruwar lamarin, jami’an hukumarmu sun gazaya wurin tare da gaggauta fara aikin ceto, inda suka zaƙulo gawarwakin mutum uku duka maza, da wasu mazan biyu da aka zaƙulo da ransu sai kuma wani mutum guda da ya maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan ginin da shi ma aka ceto shi”, in ji shi.

Ya kuma ƙara da cewa tuni aka garzaya da mutanen da aka ceto zuwa asibiti domin samun kulawar likitoci. Tuni aka kai manyan motocin tono domin faɗaɗa aikin ceton.

Rushewar gini wata matsala ce da ake yawan samu Najeriya. Ko a farkon wannan wata ma, an samu ruftawar ginin wata makaranta a jihar Filato da ke tsakiyar ƙasar, lamarin da ya yi sanadin mutuwar yara fiye da 20, tare da raunata mutane da dama.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 13 minutes 30 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 54 minutes 55 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com