Home DUNIYA Shugaban Chaina ya yaba da kamun Ludayin Tinubu a ECOWAS

Shugaban Chaina ya yaba da kamun Ludayin Tinubu a ECOWAS

Shugaban ƙasar China Xi Jinping, ya gayyaci takwaransa na Najeriya Bola Tinubu, domin kai ziyarar aiki ƙasar.

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin shugaban kasar, Ajuri Ngelale ya fitar, wadda ta ce mataimakin ministan ƙasashen wajen China, Chen Xiaodong, ne ya je da saƙon gayyatar ca wata ziyara da ya kai Najeriya.

Mista Xiaodong ya yaba wa Shugaba Tinubu kan irin tsare-tsarensa, da irin rawar da shugaban ke takawa a matsayinsa na jagoran kungiyar Ecowas.

“Kai shugaba ne mai haƙaza da fikira. Mun yi imanin cewa ganawar ka da Mista Jinping zai kawo damarmaki masu yawa ga Najeriya da Afirka,’’ in ji shi.

A nasa ɓangaren shugaban na Najeriya ya yaba wa shugaban China, bisa ƙoƙarin da yake yi na ƙarfafa alaƙa da Najeriya da ƙasashen nahiyar Afirka.

“Mun yi imani da alaƙar da ke tsakaninmu, kuma muna son yauƙaƙa danƙon zumuncin da ke tsakaninmu , musamman ta hukumomin MDD da ƙungiyar BRICS da G20.”, in ji sanarwar.

Haka kuma shugaban ya yaba da saƙon gayyatar da shugaban na China ya aika masa na ziyarar aiki zuwa China.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp