Home General Jami’oi ku lura da Lafiyar Dalibai da Ma’aikatan ku yayin zanga-zanga –...

Jami’oi ku lura da Lafiyar Dalibai da Ma’aikatan ku yayin zanga-zanga – Ministan Ilimi

Gwamantin Nijeriya ta umarci Jami’oin kasar da su Tabbatar da tsaron Lafiyar dalibai da kuma maáikata a makarantunsu yayin da ake gudanar da zanga-zangar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mukaddashin shugaban hukumar kula da jami’oin kasar, Chris Maiyaki ya fitar wacce aka rabawa manema labarai a yau Litinin bias umarnin ministan ilimin kasar Farfesa Tahir Mamman.

Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da matasa a Nijeirya ke shirin fitowa titinu domin nuna bakin ciki da haln kuncin rayuwa da suke ciki a kasar, dake da arzikin man Fetur da tarin ma’adanai.

Ta cikin sanarwar Ministan ya kuma bukaci dalibai da su kasance a makarantunsu tare da mayar da hankali ga karatunsu domin kaucewa fadawa hatsari a yayin zanga zangar.

“Gwamnatin tarayya tana sane da hakkin da kowanne dan Nijeriya ke da shi wajen gudanar da zanga zangar lumana, amma mun damu da lafiyar ma’aikata da dalibai da makarantu a yayin zanga-zanga.

” A don haka minista ya umarci dukkan shugabannin makarantu da su dau matakai don tabbatar da tsaron dalibai da ma’aikatan jami’a”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp