Ana fargabar ‘yan Sanda sun harbi masu Zanga Zanga a Kano

Masu zanga zanga a jihar Kano sun zargi jami’an tsaro da harbi kan masu mutum biyu a cikin su.

Ta cikin wata ganawa da PRNigeria ta yi da guda cikin masu zanga zangar kwamared Aliyu D. yace sun fito zanga-zangar ta lumana amma wasu cikin jami’an ‘yan sandan dake aiki domin samar da tsaro suka fara harba musu hayaki mai saka hawaye inda daga bisani kuma suka fara harbin su da bindiga.

Aliyu yace muddin aka cigaba da tafiya a haka bau dalilin da saka su koma gida sai gwamnati tayi musu abinda ya kamata, na dawo da tallafin man fetur da magance tsadar rayuwar a fadin Nijeriya.

Yayin da ake ci gaba da zanga-zanga a fadin Najeriya, dubban matasa a jihar Kano sai kara fitowa suke daga unguwanni suna taruwa a kan titin gidan gwamnati.

matasan rike da alluna suna ta furta kalmomin “Ba ma yi” wasu matasan na komawa gida suna sake shiri.

Ana fargabar an harbi mutum uku cikin masu zanga-zangar, Jami’an tsaro kuma a wasu wuraren sun zama yan kallo sannan sun janye motocin su ƙanana.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 41 minutes 54 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 23 minutes 19 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com