Kungiyar kare haƙƙin bil’Adama ta Amnesty International ta yi Allah-wadarai da samamen da jami’an tsaro suka kai hedikwatar ƙungiyar kwadago ta Najeriya, ta NLC.
Kungiyar ta ce samamen da aka kai jiya Laraba da daddare ya yi kama da wata mummunar manufa ta hantarar ƙungiyar ƙwadagon.
A cewar Amnesty International, samamen da jami’an tsaron suka kai ya tauye ƴanci da damar ma’aikata na gudanar da zanga-zanga.
A yayin samamen, jami’an tsaron sun yi awon gaba da littattafai na kungiyar NLC, tare da kwace kayayyakin da suka ce an yi amfani da su wajen tada zaune tsaye da kuma shirya zanga-zangar baya-bayan nan.
Ƙungiyar ta Amnesty ta bayyana matukar damuwarta game da tsaron jami’an NLC.
Sannan ta jaddada cewa a karkashin dokokin kare hakkin bil’Adama na ƙasashen duniya, ba a harin ƙungiyoyin ƙwadago saboda gudanar da ayyukansu.











