Home Labarai Amnesty ta magantu kan simamen jami’an tsaro shelkwatar NLC

Amnesty ta magantu kan simamen jami’an tsaro shelkwatar NLC

Kungiyar kare haƙƙin bil’Adama ta Amnesty International ta yi Allah-wadarai da samamen da jami’an tsaro suka kai hedikwatar ƙungiyar kwadago ta Najeriya, ta NLC.

Kungiyar ta ce samamen da aka kai jiya Laraba da daddare ya yi kama da wata mummunar manufa ta hantarar ƙungiyar ƙwadagon.

A cewar Amnesty International, samamen da jami’an tsaron suka kai ya tauye ƴanci da damar ma’aikata na gudanar da zanga-zanga.

A yayin samamen, jami’an tsaron sun yi awon gaba da littattafai na kungiyar NLC, tare da kwace kayayyakin da suka ce an yi amfani da su wajen tada zaune tsaye da kuma shirya zanga-zangar baya-bayan nan.

Ƙungiyar ta Amnesty ta bayyana matukar damuwarta game da tsaron jami’an NLC.

Sannan ta jaddada cewa a karkashin dokokin kare hakkin bil’Adama na ƙasashen duniya, ba a harin ƙungiyoyin ƙwadago saboda gudanar da ayyukansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp