Home Labarai Gwamnatin Kaduna ta sassauta dokar hana fita

Gwamnatin Kaduna ta sassauta dokar hana fita

Gwamnatin jihar Kaduna ta sassauta dokar hana fita da ta sanya sakamakon tarzomar da ta biyo bayan zanga-zangar matsin rayuwa, inda yanzu jama’a za su iya fita daga karfe 8 na safe zuwa 6 na yamma.

A sanarwar da kwamishinan kula da harkokin cikin gida da tsaro na jihar Samuel Aruwan ya fitar, ya ce bayan nazarin yanayi da majalisar tsaro ta jihar ta yi a yanzu ta rage lokacin dokar ta sa’a 24, wadda aka sanya ranar Litinin 4 ga watan Agusta, 2024.

Da wannan sassauci sanarwar ta ce daga yanzu jama’a za su ci gaba da kasancewa a gida daga karfe 6 na yamma har sai karfe takwas na safe sannan su fito su ci gaba da gudanar da harkokinsu.

Kwamishinan ya jadda cewa jami’an tsaro za su ci gaba da tabbatar da ganin jama’a sun kiyaye tare da bin umarnin da aka bayar na bin dokar, da tabbatar da tsaro.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp