Home Labarai Gwamnatin tarayya ta dakatar da sayar da shinkafa ga ma’aikatan Gwamnati

Gwamnatin tarayya ta dakatar da sayar da shinkafa ga ma’aikatan Gwamnati

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta dakatar da shirinta na sayar wa da ma’aikatan gwamnati buhun shinkafa mai nauyin kilogram 50 ko mai kwano 17, da ta sanar a baya a kan farashi mai rahusa – naira dubu 40.

Ma’aikatar ayyuka na musamman ce ta sanar da haka a wata takarda da ta fitar, ɗauke da sa hannun darektar kula da harkokin jama’a, Aderonke Jaiyesimi, mai kwanan wata, 2 ga watan Agustan 2024.

Sai dai takardar ba ta yi bayani kan dalilin da ya sa aka dakatar da shirin ba, ko ma an soke shi ne gabaɗaya ko kuma zuwa wani lokaci aka ɗage shi.

A shirin da aka sanar tun farko, a ranar 1 ga watan Agusta, 2024 ta wata takarda dama’aikatar da fitar, an buƙaci ma’aikatan gwamnati da ke son sayen shinkafar da su je shafin intanet na ofishin shugaban ma’aikata na tarayya su cike wata takarda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp