Home General Kotu ta tura jagororin Zanga-Zanga gidan gyaran hali a jihar Katsina

Kotu ta tura jagororin Zanga-Zanga gidan gyaran hali a jihar Katsina

Wata kotu a jihar Katsina ta tura 7 daga cikin jagororin zanga-zangar tsadar rayuwa da aka yi a ƙasar, gidan yari tsawon wata ɗaya.

Wani makusancin biyu daga cikin jagororin ya shaodawa kafar BBC cewa, a ranar Juma’a 9 ga watan Agusta 2024, rundunar ‘yansanda ta jihar ta gurfanar da Kwamared Habibu Ruma da Kwamared Kabir Shehu ‘Yanɗaki da kuma wasu mutum biyar a gaban kotun majistare a birnin Katsina, inda ta tuhume su da laifukan da suka haɗa da tarzoma da sata da kuma ɓarnata kayan gwamnati.

Bayan an karanta musu laifukan da ake tuhumarsu da su, ”sai kotun ta ɗage zamanta zuwa ranar 11 ga wata mai zuwa, Satumba, 2024 tare da bayar da umarnin a ci gaba da tsare mutanen bakwai a gidan kaso, zaman waƙafi.

A Najeriya an gudanar da zanga-zanga ta gama-gari daga ranar 1 ga watan Agusta, 2024 zuwa 10 ga watan na Agusta 2024, saboda matsaloli da suke addabar ƙasar, waɗanda suka haɗa da tsadar rayuwa da rashin tsaro musammana a arewacin da neman shugabanci na gari.

Sai dai yayin da zanga-zangar ta kasance cikin lumana a wasu jihohin, a wasu kuwa ta rikiɗe ta zama tarzoma inda aka riƙa sace-sace da ɓarnata kayan gwamnati da na ‘yan kasuwa da ɗaiɗaikum mutane.

Tarzomar ta kuma yi sanadin kashe mutane da jikkata wasu da dama.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp