Home Labarai Ba a ba mu umarnin fara biyan masu yi wa ƙasa hidima...

Ba a ba mu umarnin fara biyan masu yi wa ƙasa hidima N70,000 ba – NYSC

Hukumar da ke Kula da Matasa Masu yi wa Kasa Hidima (NYSC) ta ce ba ta umarci matasa masu hidimar ƙasa su gyara asusun ajiyarsu na bankuna domin ta fara biyan su N70,000 ba.

NYSC dai a yanzu haka tana biyan matasan Naira 33,000 a kowanne wata a matsayin kuɗaɗen alawus-alawus.

Hukumar ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da Daraktanta na yaɗa labarai, Eddy Megwa, ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

A cewar sanarwar, yanzu haka kururuwar na nan ta karaɗe shafukan sada zumunta na zamani, inda ta ce amma ƙarya ce tsagwaronta.

Eddy ya kuma ce, “Muna sanar da matasa masu yi wa ƙasa hidima, iyaye da sauran jama’a cewa har yanzu ba mu karɓi umarni daga sashen gwamnati da ke kuka da batun biyan albashi ba a kan lamarin.

“Saboda haka, ba zai yiwu NYSC mu bayar da wani umarni ba a kan lamarin.

“Matasa masu yi wa ƙasa hidima sun san hanyoyin da muke bi idan za mu fitar musu da sanarwa, don haka su yi watsi da wannan maganar.

“Daga wannan sanarwar, muna ba matasan shawara da su daina yarda masu neman tayar da zaune tsaye suna wasa da hankulansu,” in ji shi.

A ƙarshen watan da ya gabata ne dai Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya rattaba hannu a kan sabuwar dokar mafi ƙarancin albashi wanda yanzu ya koma Naira 70,000.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp