Home Labarai Gwamnatin Kano ta janye dokar hana fita gaba daya a jihar

Gwamnatin Kano ta janye dokar hana fita gaba daya a jihar

Gwamnan jihar Kano ya sanar da janye dokar hana fita da ya saka sakamakon tarzomar da ta biyo bayan zanga-zanga kan matsin rayuwa a Nijeriya.

Abba Kabir Yusuf ya sanar da matakin ne yayin da yake yi wa ‘yanjarida jawabi a jihar yau Litinin bayan wata ziyarara gani da ido da ya kai harabar kotun da matasa suka yi barna a ranar zanga-zangar.

“Gwamnati ta janye wannan doka gaba ɗaya, kuma mai girma gwamna ya jinjina wa malamai da jami’an tsaro da suka jajirce don ganin an samu zaman lafiya,” kamar yadda Kwamashinan Yaɗa Labarai Baba Halilu Dantiye ya shaida wa manema labarai cikin wani saƙon murya.

Gwamnati ta saka dokar a ranar 1 ga watan Agusta bayan wasu ɓata-gari sun auka wa gine-gine da shagunan mutane tare da yin wawashe kayayyaki a ranar farko ta zanga-zangar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp