Home Labarai Tinubu yana iya bakin kokarinsa – T Gwarzo

Tinubu yana iya bakin kokarinsa – T Gwarzo

Karamin ministan gidaje da raya birane na Nigeria Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo ya tabbatarwa ‘yan Najeriya cewa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu yana bakin kokarinsa wajen gyara matsalolin kasar.

Ministan ya bada wannan tabbacin ne a lokacin da ya karbi bakuncin mambobin kungiyar APC 4G Forum na Kano da suka kai masa ziyarar ban girma a ofishin sa.

Ya bayyana cewa a halin yanzu shugaban kasar ya kaddamar da ayyuka da dama wadanda aka samar da su da niyya magance matsalolin da ke addabar al’umma.

Minista Gwarzo ya yi kira ga ’ya’yan kungiyar APC 4G Forum na Kano da su tabbatar da hadin kan jam’iyyar tare da bayar da gagarumar gudunmuwa don samun nasarar Shugaba Bola Ahmad Tinubu a yunkurinsa na sake dawo da kasar nan kan saiti.

Ya kuma shawarci kungiyar da ta hada kan dukkan ‘ya’yan jam’iyyar karkashin inuwa daya domin gujewa maimaita kurakuran da aka yi a baya. Ya kara da cewa ya kamata kowa ya tashi tsaye domin tallata gwamnatin Bola Tinubu.

Tun da farko, Shugaban rikon kungiyar APC 4G Forum na Kano, Kwamared Sale Jeli (Sarkin Fadar Karaye) ya bayyana nagartar Ministan, inda ya bayyana shi a matsayin jagora na gari mai kishin kasa, wanda a kodayaushe ya ba da fifiko wajen yi wa al’ummarsa hidima.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp