Home Labarai Sojojin Nijeriya zasu gudanar da bincike kan abin ya faru a Kaduna

Sojojin Nijeriya zasu gudanar da bincike kan abin ya faru a Kaduna

Babban hafsan sojin ƙasa na Nijeriya, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin da ya faru a kasuwar Sabon Birni da ke jihar KAduna domin gano haƙianin abinda ya faru, da kuma kamo wadanda ake zargi.

Cikin wani bidiyo da aka yaɗa a shafukan sada zumunta, an ga yadda wasu da aka yi zargin sojoji ne sun kashe mutum uku tare da shanu a ƙalla 100 a kasuwar Sabon Birni da ke yankin ƙaramar hukumar Igabi a jhar Kaduna.

To sai dai cikin wata sanarwa da rundunar sojin ƙasa ta Nijeriya ta fitar ta hannun daraktan yaɗa labaranta, Onyema Nwachukwu, ta jajanta wa iyalan al’ummar yankin Sabon Birni da mutanen da lamarin ya shafa, tare da alƙawarta gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

”Kuma duk jami’in da muka samu da hannu a wannan lamarin, to za mu ɗauki matakin da ya dace a kansa”, kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

Sanarwar ta ci gaba da cewa kundin tsarin mulkin Najeriya ya ɗora wa rundunar sojin ƙasa ta Najeriya alhakin kare rayuka da dukiyoyin al’umma, don haka ba za ta lamunci duk wani yunƙurin saɓanin hakan ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp