Home General Gwamnan Kano ya bayar da umarnin Rufe Asusun Ma’aikatu da hukumomin Gwamnatin...

Gwamnan Kano ya bayar da umarnin Rufe Asusun Ma’aikatu da hukumomin Gwamnatin jihar

Gwamnan ya bayar da umarnin rufe dukkanin asusun ma’aikatu da hukumomin gwamnati domin aiwatar da tsarin asusun bai daya Wanda Zai tabbatar da Sanin Kudade da Suka Shiga da Kuma fita Daga asusun Gwamnatin Jihar Kano

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana haka yayin da yake kaddamar da tsarin tattara kudaden haraji da aiwatar da asusun bai daya ajihar Kano wanda hukumar tattara kudaden haraji ta jiha ta aiwatar.

Gwamna Abba wanda ya nuna damuwarsa kan yadda kudaden harajin jihar Kano suke zirarewa ya ce gwamnatin jiha ta aiwatar da tsarin ne domin dakile hanyoyin zirarewar kudi wanda zai bawa gwamnati damar gudanar da ayyukan raya kasa da cigaban al’uma.

Haka Kuma Gwamnan Ya ja hankalin shugabannin hukumomi da ma’aikatalun jiha dasu yi biyayya ga sabon tsarin, yana Mai jadda cewa gwamnatin jiha zata dauki matakin ladabtarwa ga duk Wanda suka ki yin biyya ga tsarin.

Shugaban hukumar tattara kudaden haraji ta jiha Dr. Zaid Abubakar Yace abin takaici ne yadda jihohin Lagos da River suka yi wa jihar Kano zarra duk da kasancewar Jihar Kano amatsayin cibiyar kasuwanci a kasar nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp