Home General Atiku ya caccaki manufofin Tinubu kan ƙayyade shekarun shiga jami’a

Atiku ya caccaki manufofin Tinubu kan ƙayyade shekarun shiga jami’a

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya yi kakkausar suka ga manufar ma’aikatar ilimi ta tarayya na kayyade shekarun shiga jami’o’i, inda ya bayyana hakan a matsayin wani baƙon abu da zai janyo komabaya ga harkar ilimi a Najeriya

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, Atiku ya bayyana manufar a matsayin “zai haifar da naƙasu ga hakar ilimi” inda ya ce hakan ya saɓa wa ƙa’idojin tsarin ƙasar ta hanyar shiga ayyukan gwamnatocin jihohi.

Atiku ya yi nuni da cewa ilimi na cikin abubuwan da ke cikin ƙundin tsarin mulkin Najeriya, wanda ya bai wa ƙananan hukumomin ƙasar karfi wajen tafiyar da harkokinsa.

Ya yi allah-wadai da matakin da gwamnati ta ɗauka na kafa manufofin ilimi ba kamar yadda doka ta tanada ba inda ya bayyana cewa hakan ya saɓa wa ƙundin tsarin mulkin ƙasa da kuma ɓata tsarin gwamnati.

Atiku ya ce, ‘Wannan sabon tsari na gwamnati ba zai yi tanadi ga dalibai masu hazaƙa ba wanda hakan ke nuna rashin mutunta hazaƙar ilimi.”

“Ya kamata gwamnati ta mayar da hankali wajen zaƙulo ɗalibai masu hazaƙa tare da tallafa musu, ba tare da la’akari da shekarunsu ba” Atiku ya kara da cewa.

Atiku ya buƙaci da a bar wa gwamnatocin jahohi kula da harkokin ilimi, wanda a tunaninsa zai fi dacewa da yadda ake yi a ƙasashen duniya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp