Home General Gwamnan Kano ya kwace kwangilar Titin Garko mai tsawon kilomi 5

Gwamnan Kano ya kwace kwangilar Titin Garko mai tsawon kilomi 5

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ziyarci Dam din Kafinchiri a karamar hukumar Garko, domin ganin yadda aiki ke gudana, wanda aka bayar da shi a yunkurin kawo sauyi a fannin noma a jihar.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ranar Lahadi.

Sanarwar tace aikin, wanda darajarsa ta kai Naira biliyan 2.5, an yi shi ne da nufin bunkasa noman rani da damina, da inganta samar da abinci, da kuma bunkasa tattalin arzikin jihar.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada muhimmancin aikin noman na Kafinchiri, inda ya bayyana hakan a matsayin wani muhimmin bangare na kokarin gwamnatinsa na bunkasa noma a jihar Kano.

Ya bukaci mazauna garin Garko da kewaye da su yi amfani da damar da aikin zai bayar domin inganta tattalin arzikin su da jihar baki daya.

A wani labarin kuma, Gwamnan ya sanar da kwace kwangilar aikin hanyar karamar hukumar Garko mai tsawon kilomita biyar saboda gazawar dan kwangilar na dawowa bakin aiki.

Ya ba da tabbacin cewa nan ba da jimawa ba za a baiwa wani mai kwazo kwangilar aikin don tabbatar da kammala aikin a kan kari.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kuma kuduri aniyar samar da cibiyar lafiya ta zamani a garin Garko, da nufin kusantar da harkokin kiwon lafiya ga jama’a.

Ya nuna jin dadinsa bisa goyon bayan da al’ummar yankin suke ba shi tare da jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba gudanar da aiyukan cigaba a jihar .

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp