Home General Tinubu ya ƙara wa babban sufeton ‘yan sandan Najeriya wa’adin shekaru 3

Tinubu ya ƙara wa babban sufeton ‘yan sandan Najeriya wa’adin shekaru 3

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da ƙarawa Babban Sefotun ‘yan sandan kasar Kayode Egbetokun wa’adi, kamar yadda wata majiya daga ofishin sakataren gwamnatin tarayya ta bayyana.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito an ƙara wa shugaban ‘yan sandan wa’adin shekara uku ne, ma’ana sai zuwa 2027.

Ta ruwaito cewa Sakataren Gwamnatin Tarayya George Akume ne ya bai wa Babban Sufeton ‘yan sandan takartar ƙara masa wa’adin a ranar Litinin.

A watan Yulin da ya gabata ne Majalisar Dattijan Najeriya ta yi garambawul ga dokar ‘yan sanda ta 2020 ƙarƙashin sashe na 8, wadda ta ci karo da ƙarawa ma’aikacin gwamnati wa’adin aiki bayan shekara 35 ko kuma bayan kaiwa shekara 60 a raye.

Egbetokun wanda aka naɗa IG a watan Yunin 2023 zai cika shekara 60 ne a gobe 4 ga watan Satumba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp