Home General Sojojin Najeriya sun kama masu kai wa ‘yan bindiga makamai a kasar

Sojojin Najeriya sun kama masu kai wa ‘yan bindiga makamai a kasar

Wasu rahotannin daga Nijeriya na bayyana cewa dakarun Sojojin kasar tare da takwarorinsu na tsaro sun kama wasu mutane 15 da ake zargi da samar wa ‘yan bindiga makamai da sauran kayan aiki.

Wannan na cikin wata sanarwa da sojojin suka wallafa a shafinsu na X, inda suka ce an yi kamen ne bayan samun bayanan sirri kan mutane.

Sanarwar ta ƙara da cewa an kashe wani mutum guda da ake zargin ɗan bindiga ne yayin wannan samamen a wurare da dama.

A yayin saman dakarun kasar sun yi nasarar kama makamai masu dama da alburusai da kuma wasu kayayyaki na daban.

“A ranar 30 ga watan Agusta 2024, dakaru sun kai hari kan ‘yan bindiga da masu yi musu jigilar kayayyakinsu a Mararaba Donga da ƙauyen Manya da suke a Ƙananan hukumomin Donga da Takum a jihar Taraba.

“An kama mutum biyar da ake zargi a lokacin samamen, an kuma kamaya kayayyaki kamar haka: bindiga uku ƙirar AK-47, bindiga biyu ƙirar cikin gida, bindiga biyu ƙirar da ba ta gida ba, bindiga biyu ta farauta, wata bindiga mai ɗaukar harsashi 61 da dai sauransu.

“A Yobe dakarun sun kama wasu masu kaiwa mayaƙan Boko Haram kayan aiki a ƙauyen Jimbal da ke ƙaramar Hukumar Tarmuwa.

“A Kaduna an kama makamantan waɗannan mutane masu kai kayan aiki a ƙauyen Rijana a ƙaramar Hukumar Chikun. Tare da su akwai wayoyi uku da ke da katin waya sama da naira 100,000, an kuma samun garin kuɗi naira 1,532,900.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp