Home General Majalisar jihar Kano ta Amince da kudirin kara kasafin kudin jihar

Majalisar jihar Kano ta Amince da kudirin kara kasafin kudin jihar

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da kudirin kara kasafin kudin jihar da naira biliyan 99.2

Kudirin ya samu karbuwa daga dukkan kwamitin majalisar baki daya bayan kammala karatu na uku a zauren majalisar a ranar Alhamis.

Gwamna Abba Yusuf ya gabatar da kudirin dokar ne a ranar 26 ga Agusta, 2024 inda ya nemi a kara kasafin kudin zuwa Naira biliyan 536, 559, 816, 357.84 maimakon Naira biliyan 437, 338, 312, 787 da aka sanya wa hannu a watan Disamba 2023.

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala zaman majalisar, shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar, Hon. Aminu Sa’ad, ya bayyana cewa, kashi 58 cikin 100 na kasafin kudin an ware su ne domin manyan ayyuka na more rayuwa yayin da kashi 42 cikin 100 kuma aka ware domin gudanar da ayyukan yau da kullum.

Hon. Sa’ad ya kara da cewa, karin kasafin kudin an yi shi ne domin aiwatar da zabukan kananan hukumomi da ke tafe, biyan sabon mafi karancin albashi, kudaden gudanarwa ga sabbin ma’aikatun da aka kafa da sake bude cibiyoyin koyar da sana’o’i da sauran ayyukan da gwamnati ta sa gaba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp