Home General Kotu ta ba da belin masu zanga-zangar tsadar rayuwa kan miliyan 10

Kotu ta ba da belin masu zanga-zangar tsadar rayuwa kan miliyan 10

Wata kotu a Abuja babban birnin Najeriya ta bayar da belin mutum 10 da ake tuhuma da cin amanar ƙasa yayin zanga-zanga kan tsadar rayuwa.

Mai Shari’a Emeka Nwite ya ce ya ba da belin maza tara da mace ɗaya, waɗanda ba su amsa tuhumar da ake yi musu ba kan naira miliyan 10 kowannensu.

Cikin tuhume-tuhumen da ake yi musu har da haɗa baki wajen tunzira sojoji su kifar da gwamnatin Bola Tinubu a zanga-zangar da suka gudanar a watan Agusta.

Sai dai tun da farko masu shigar da ƙara sun nemi kotun ta yi watsi da neman belin a makon da ya gabata.

Waɗanda ake zargin na iya fuskantar hukuncin kisa idan aka kama su da aikata laifukan da ake tuhumar su.

Alƙalin ya ɗage cigaba da sauraron ƙarar har zuwa ranar 27 ga watan Satumba. Sai dai ƙungiyar kare haƙƙi ta Amnesty International ta nemi gwamnati ta sake su ba tare da wani sharaɗi ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp