Home General Mun dakile hari kan kayan hukumar DSS – Sojojin Najeriya

Mun dakile hari kan kayan hukumar DSS – Sojojin Najeriya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar da cewa ta daƙile yunƙurin ƴan ta’adda a Jihar Neja daga kai hari a kan kadarorin Hukumar DSS.

Wata majiyar tsaro ta shaida wa PRNigeria cewa sojojin, da taimakon jirgin Super Tucano na sojojin sama sun yi nasarar kashe wasu ƴan ta’addan da suka kai harin.

Majiyar wadda ta nemi a ɓoye sunanta ta ce lamarin ya faru ne a garin Bassa a ƙaramar hukumar Shiroro na jihar.

A cewar majiyar, sojojin sun samu nasara a kan ƴan ta’adda bayan samun bayanan sirri a kan shirinsu na kai harin a kan kayayyakin DSS.

“Nan da nan aka tashi jiragen Super Tucano, inda suka samu nasarar daƙile yunƙurin na ƴan bindigan. Sannan harin jirgin ya kashe aƙalla ƴan bindiga 30,” inji majiyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp