Home General Sojojin Najeriya sun hallaka kwamanda ISWAP “Ibn Kaseer” a Borno

Sojojin Najeriya sun hallaka kwamanda ISWAP “Ibn Kaseer” a Borno

Dakarun sojin Nijeirya karkashin  rundunar Operation hadin kai ta sami nasarar hallaka kwamandan mayakan kungiyar ISWAP, Ibn Kaseer tare da wasu mayakan kungiyar guda uku a wani hari da suka kai dajin Sambisa a safiyar ranar Alhamis.

Zagazola makama ya bayyana cewa wani rahoton sirri ya tabbatar da yadda dakarun sojojin karkashin rundunar sojoji ta 21, sun sami nasarar a yayin wata kora da suka kai a kauyen Kashomeri.

Kwamandan mayakan na ISWAP ta ya addabi al’ummar Geizuwa da Yale ya yi yunkurin samun mafaka a yankin na Kashomeri shi da iyalansa.

Majiyar dai ta tabbatar da cewa bayan bankado maboyar ta sa ne dakarun suka hallaka shi tare da wasu mayakansa guda biyu da aka bayyana a matsayin Bulamadu, sai dai majiyar tace lamarin ya faru ne bayan da mutanen sa suka fita wani aikin taaddanci a yankin Jalumeri.

Haka kuma bayan hallaka kwamandan rundunar ta sami nasarar kubutar da mata hudu da yara kanana, yayin da wasu daga cikin ‘iyalan mayakan na ISWAP suka mika wuya ga dakarun sojojin a Kunduga.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp