Home AFIRKA Harin masu tada kayar baya a Mali ya kashe mutum 70 da...

Harin masu tada kayar baya a Mali ya kashe mutum 70 da jikkata wasu 200

Wani harin mayaƙa masu iƙirarin jihadi da aka kai sansanin horar da sojoji da filin tashi da saukar jiragen sama na babba birnin Mali, Bamako ya yi sanadin mutuwar sama da mutane 70 tare da jikkata 200, adadi mafi muni na jami’an tsaro da aka taɓa samu a shekarun baya-bayann nan.

Wata majiyar tsaro da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa mutanee 77 ne suka mutu, kana 255 suka samu raunuka a harin da aka kai Bamako a ranar Talata.

Zalika, wani bayanin sirri na hukuma da aka tantance sahihancinsa ya ce adadin waɗanda suka mutu ya kai kimanin ɗari, inda ya bayyana sunayen 81 daga cikin su.

Jaridar Le Soir da ake wallafawa a kasar ta ranar Alhamis ɗin nan ya ruwaito cewa a ranar aka yi jana’izar kimanin dakaru masu karɓar soji kimanin 50.

Har ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto mahukuntann gwamnatin sojin Mali ba su fitar da ainihin adadin waɗanda su ka mutu  a harin da ƙungiyar mayaƙa masu iƙirarin jihadi da ke da alaƙa da Al-Qaeda ta ɗauki alhakin kai wa ba.

Ƙwararru sun ce harin sshi ne naa farko irin sa a cikin shekaru, kuma ta yi mummmunan tasiri a kan gwamnatin sojin ƙasar.

Ba a cika samun hare-hare a babban birnin ƙasar Mali  kamar yadda ake samu a sauran sassan ƙasar kusan kullayaumin ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp