Home Labarai Sanata Ndume ya bukaci Tinubu ya tausayawa ‘yan Nijeriya

Sanata Ndume ya bukaci Tinubu ya tausayawa ‘yan Nijeriya

Ɗan majalisar dattijan Najeriya mai wakiltar Borno ta kudu, Sanata Ali Ndume ya yi kira ga shugaba Bola Tinubu da ya rage farashin man fetur, inda ya ce ƴan Najeriya na cikin wahala.

Ndume ya bayyana haka ne yayin tattaunawa da manema labarai a Abuja, inda ya kuma ce ci gaba da ƙara farashin man fetur da abinci da kuma kayan amfani na yau da kullum na ƙara jefa ƴan Najeriya cikin kunci da wahala, musamman ma talakawa.

Tsohon mai tsawatarwa na majalisar ya ce wasu ɓata-gari cikin gwamnati na ƙoƙarin haddasa fitina tsakanin mutane da gwamnatin Tinubu ta hanyar ɓullo da tsare-tsare masu tsauri da kuma mara kyau maimakon shawo kan matsalar hauhawar farashi da kuma tashin kuɗin dala da ke ci gaba da kassara ƴan ƙasar.

“Wasu ne kawai ke son ɓata Tinubu a idon jama’a ta hanyar ɓullo da waɗannan tsare-tsare daga karshe kuma laifi ya koma kan shugaban.

“Ina kira ga shugaban ƙasa da ya daina kula waɗannan mutane da ke son kawo cikas ga gwamnatinsa.Halin kunci da mutanen ke sa ƴan Najeriya ba zai misaltu ba,” in ji Ndume.

Ya ce mutane na cikin matsanancin wahala musamman ma jihar sa ta Borno.

“Mutane na cikin matsi, akwai yunwa, ɓacin-rai da kuma fushi cikin al’umma,” in ji Sanatan.

Ya ce ya san shugaba Tinubu yana da manufa mai kyau ga ƴan Najeriya, sai dai wasu masu ba shi shawara ne ke son kassara ƴan ƙasar ta hanyar ba shi shawara mara amfani.

Sanata Ndume ya buƙaci shugaban ƙasar da ya duba batutuwan da zarar ya koma daga hutun da ya tafi da nufin shawo kan su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp