Home General Gwamnatin Kano ta tallafawa wadanda gobara ta shafa a jihar Jigawa

Gwamnatin Kano ta tallafawa wadanda gobara ta shafa a jihar Jigawa

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya tallafawa mutanen da iftila’in fashewar tankar mai ya shafa a garin Majiya dake karamar hukumar Taura a jihar Jigawa da kyautar naira miliya 100.

Gwamnan ya bada tallafin ne lokacin da ya kai ziyarar ta’aziyya da jaje ga al’ummar jihar Jigawa bisa wannan ibtila’i wanda ya yi sanadiyyar rasa rayuka sama da 160 da kuma jikkata al’umma da dama.

Gwamna Abba ya miƙa ta’aziyyarsa a madadin gwamnati da al’ummar jihar Kano tare da fatan Allah ya kare afkuwar hakan a nan gaba.

Har ila yau gwamnan ya ƙara da cewa ibtila’in ba iya al’ummar jihar jigawa kaɗai ya shafa ba, har ma da al’umar jihar Kano, la’akari da dangantakar dake tsakanin jihohin biyu.

Daga nan ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suku rigamu gidan gaskiya ya bawa waɗanda suka jikkata lafiya.

A nasa bangaren, gwamnan jihar Jigawa Alhaji Umar Namadi Ɗanmoɗi ya godewa gwamna Abba Kabir Yusuf bisa ziyarar jaje da ta’aziyyar da ya kaiwa al’ummar jihar, inda ya ce ziyarar zata kara karfafa dangantakar dake tsakanin jihohin biyu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp