Home General Kananan Yara a Jihar Kano na cikin hadarin kamuwa da cutar Polio

Kananan Yara a Jihar Kano na cikin hadarin kamuwa da cutar Polio

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci al’ummar jihar da su tabbatar an yiwa yaran su allurar rigakafin cutar inna wato Polio, domin gujewa yaduwar cutar a cikin al’umma.

Kwamishinan lafiya na jihar Dr. Abubakar labaran Yusuf ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai, a wani bangari na bikin ranar yaki da cutar ta Shan inna a jihar Kano.

Dr. Abubakar labaran ya ce wannan rana na da matukar muhimmancin wajen tunatar da al’ummar yadda wannan cuta ke kassara dan adam da zarar ta shiga jikin sa.

“Mun hadu yau 24 ga watan 10 na  shekarar 2024 domin mu tunatar da kan mu, muhimmancin wannan rana da aka ware musamman saboda cutar shan inna”

“ita wannan cuta, cuta ce wadda kwayar cuta da ake kira “Poliovirus” take janyowa, wadda idan ta shiga jikin dan Adam take janyo nakasu, take bin laka ta jikin dan Adam ta kassarashi, wani ta janyo masa rashin kafa wani rashin hannun, wani ma hannun da kafafuwan su shanye”.

Ya kara da cewa wajibi ne akan ma’aikatan lafiya a jihar kano su tabbatar da an kawar da cutar, daga cikin al’umma domin kaucewa hadarin da take dauke da shi.

“Wannan aiki abu ne mai yiwuwa, kuma za’a iya yin sa, domin ya zama dole akan mu, mu ma’aikatan gwamnati, ma’aikatan lafiya ‘yan jarida da kuma iyaye wanda Allah ya dora musu Alhakin tabbatar da cewa sun samawa ‘ya’yansu makoma mai kyau”

Ya kuma ce tuni cutar ta bar jihar kano, bisa kokarin gwamnatin jihar na tabbatar da an inganta hanyoyin yaki da cutar, musamman ta hanyar hadaka da kungiyoyin duniya, irin sun Melinda Gate, wanda hakan yayi tasirin gaske wajen magance cutar a jihar.

Sai dai kwamishinan yace a ‘yan tsakanin an sami alamun bullar cutar a jihar Kano, wanda kuma suke zargin wasu baki ne suka shigo da ita jihar; Wanda yace kananan yara na jihar na cikin hadarin kamuwa da cutar muddin ba’a dauki matakin da ya dace ba.

“Wannan dalilin ne yasa muka ga dole mu sanar da al’umma, kuma mu yi kira garesu cewa su tabbatardukkanin yara musamman wadanda ke kasa da shekaru 5 a duniya da zarar jami’an dake allurar sun isa inda yaran suke”.

Daga bisani ya tabbatar da cewa yaran da aka samu sun kamu da wannan cuta, basu haura shekaru biyar zuwa bakwai a duniya ba, wanda hakan ke da nasaba da rashin mayar da hankali a yin allurer ta rigakafin cutar shan inna.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp