Home Labarai NASSI ta bude hanyar neman Rancen Naira biliyan 75

NASSI ta bude hanyar neman Rancen Naira biliyan 75

Ƙungiyar masu ƙanana da matsakaitan Masana’antu ta Najeriya, wato Nigerian Association of Small Scale Industrialists (NASSI), ta bude hanyar neman rancen Naira Bilyan 75 da Gwamnatin Najeriya ta sahale musu.

Shugaban Kungiyar na kasa Chief Dakta Solomon Daniel Vonfa ne ya sanar da hakan, a yayin wani taron manema Labarai da ya jagoranta a Shelkwatar Kungiyar dake Babban Birnin tarayya Abuja, inda ya ce a yau suka bude shafin domin Mambobin kungiyar dama dukkan al’ummar Najeriya su nema.

Hanyar neman rancen ita ce “https://fgnboimsmeinterventionloan.boi.ng/ ” a inda wadanda zasu nema ta hannun Kungiyar kuma zasu fara yin rijista da kungiyar ta shafin “https://portal.nassi-ng.org/”.

Da yake karin haske, Babban Ma’ajin kungiyar na kasa, Dakta Abubakar Tanko Bala ya ce ga dukkan masu bukatar wannan rance zasu iya nema ta waccan hanya ko kuma su ziyarci Ofishin Kungiyar NASSI mafi kusa da shi.

Kungiyar ta kuma shawarci Mambobin ta dama dukkan al’ummar kasar da suyi amfani da wannan dama, domin bunkasa kasuwancin su dama samar karin kudin shiga ga kasar dama habbaka tattalin arzikin ta.

Taron manema Labaran ya sami halartar masu ruwa da tsakin Kungiyar na sassan Kasar dama tawagar Manyan Jami’an Bankin Masana’antu na Najeriya wato Bank of Industry, karkashin Jagorancin Hajiya Amina Habu.

A ranar 16 ga watan Oktobar nan ne Gwamnatin Najeriya ta amince da bawa mambobin kungiyar rancen Naira Bilyan 75, ta hannun Bankin Masana’antu domin su bunkasa kasuwancin su dama farfado da tattalin arzikin kasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp