Home General Kace-Nace ya barke tsakanin IPMAN da Dangote

Kace-Nace ya barke tsakanin IPMAN da Dangote

Ƙungiyar dillalan man fetur ta ƙasa IPMAN, ta ce mambobinta ba sa samun loda fetur a matate man fetur ta Dangote duk da cewa sun biya naira biliyan 40 ga kamfanin NNPCL.

Shugaban IPMAN, Abubakar Garima ne bayyana haka a tashar Channels, inda ya ce sun yi mamaki da suka ji Dangote yana cewa dillalan man fetur ba sa zuwa matatarsa sayen mai.

“Idan zai sayar da mai kai-tsaye, za mu saya saboda dole sai mun biya, za a ba mu man. Yanzu haka akwai kuɗinmu naira biliyan 40 a wajen NNPCL, amma ba ma samun kayan. Kwanan nan wasu mambobinmu da NNPCL ta tura matatar Dangote, inda motocinsu suka kwashe kwana huɗu a can ba tare da sun samu man ba.”

A ranar Talata ce dai Alhaji Aliko Dangote ya gana da shugaban ƙasa Bola Tinubu, inda ya bayyana wa manema labarai bayan ganawar cewa yana litar mai sama da miliyan 500 a ajiye, amma dillalan man ba sa sayen fetur ɗin.

A ƙarshe, shugaban IPMAN, ya yi kira ga Dangote da ya duba farashin man matatarsa, sannan ya kwatanta da farashin man na ƙasashen waje. “Shin farashin ya haura na farashin da ake samu daga ƙasashen waje ko ɗaya ne? sannan wane lokaci fetur ke ɗauka kafin ya isa ga dillalin.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp