Home General Ƴansanda sun gurfanar da masu zanga-zanga kan cin amanar ƙasa a jihar...

Ƴansanda sun gurfanar da masu zanga-zanga kan cin amanar ƙasa a jihar Borno

Rundunar ƴansandan Najeriya reshen jihar Borno ta gurfanar da mutum 19 da suka haɗa da wasu ƙananan yara uku a gaban kotu bisa zargin hannunsu a zanga-zangar tsadar rayuwa a watan Agusta.

An gurfanar da su ne a gaban Mai Shari’a Aisha Mohammed Ali a babbar kotun jihar da ke birnin Maiduguri a yau Litinin.

Wannan dai na zuwa ne a dai dai lokacin da ake matsa wa gwamnatin tarayya lamba kan ta janye tuhumar da ake yi wa ƙananan yara da aka kama saboda gudanar da zanga-zangar.

A cewar takardar da aka gabatar a kotun, yaran uku suna tsakanin shekaru 14 zuwa 17.

Gwamnatin jihar Borno ta gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kuliya bisa tuhume-tuhume biyu da suka haɗa da cin amanar ƙasa, da kuma amfani da kafafen sada zumunta wajen ɓata sunan gwamnan jihar, da kuma tunzura jama’a a su yi wa gwamnati karan-tsaye.

A cewar masu gabatar da ƙara, yaran suna daga cikin mutum bakwai da suka haɗa baki wajen kafa wata ƙungiya mai suna “Zanga-zanga” ta dandalin sada zumunta na WhatsApp da Tiktok, inda ake zargin sun amince da ɗaukar makamai, wanda ya saɓa wa sashe na 79 na dokar jihar Borno ta 2023.

Kazalika, an tuhumi wasu mutane 11 da laifin ɗaga tutar Rasha a bainar jama’a, amma sun musanta zarge-zargen.

Mai shari’ar ta dage sauraron ƙarar zuwa ranar 18 ga watan Nuwamba, inda ta bayar da umarnin kai yaran wuraren tsare yara masu laifi, yayin da za a ci gaba da tsare manyan cikinsu a gidan yara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp