Home General ‘Yansandan Kano sun kama waɗanda ake zargi da garkuwa da mutane

‘Yansandan Kano sun kama waɗanda ake zargi da garkuwa da mutane

Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta ce ta kama wasu mutane da take zargi sun shiga jihar ne da nufin yin yin garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, kakakin rundunar, Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce an kama mutanen a garin Kwanar Dangora, kuma yanzu suna hannun ‘yansanda, bayan da ya ya ce sun shiga jihar da nufin yin garkuwa da mutane.

Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce ”wannan kasuwancin fa na satar mutane ba zai yi tasiri a Jihar Kano ba Insha Allah”.

Ya kuma gode wa al’ummar jihar bia addu’o’in da ya ce suna yi a koyause.

Jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya, ba ta cikin jihohin yankin da ke fama da masu garkuwa da mutane, kodayake ana ɗan samu jifa-jifa, amma ba kamar sauran wasu jhohin yankin, da matsalar ta yi ƙamari ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp