Home General Babban Sufeton Ƴansanda ya hana Amotekum aiki a zaɓen gwamnan Ondo

Babban Sufeton Ƴansanda ya hana Amotekum aiki a zaɓen gwamnan Ondo

Babban Sufeton ƴansandan Najeriya Kayode Egbetokun ya haramta wa ƙungiyar tsaro ta jihohin kudu maso yamma da ake wa lakabi da Amotekun da ‘yansintiri na Vigilante da sauran ire-irensu shiga harkokin zaɓen gwamnan jihar Ondo.

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan na ƙasa Auyiwa Adejobi ya fitar a yau Lahadi, ya ce Babban Sufeton ya bayar da umarnin tura jami’an ‘yansanda daga ɓangarori daban-daban na rundunar domin aikin zaɓen.

Aƙalla jam’iyyu 17 ne aka bayar da rahoton cewa za su shiga zaɓen wanda za a yi ranar Asabar mai zuwa, 16 ga watan Nuwamba, 2024.

Sanarwar ta ce ‘yansanda da sauran hukumomin tsaro na tarayya ne za su aikin tabbatar da tsaro a lokacin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp