Home General Dalilin Gwamnatin Kano na fara kamen kananan yaran dake yawo a titi

Dalilin Gwamnatin Kano na fara kamen kananan yaran dake yawo a titi

Gwamnatin jihar Kano ta ƙaddamar da wani kwamiti da zai yi aiki kwashe yaran da ke gararamba a titunan birnin.

Hukumomi sun ce ɗaukar matakin ya zama wajibi kasancewar barin yara ƙanana suna yawo a tituna babbar barazana ce ga tsaro da kuma ci gaba al’umma.

Kwamitin zai kuma bai wa gwamnati shawarar kan yadda za a mayar da yaran garuruwan da suka fito.

Kwamitin ƙarkashin shugabancin kwamandan hukumar Hisba, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa zai bi diddigi tare da zaƙulo yaran da suke yawo a kwararo da tituna suna kwana a kasuwanni da ƙarƙashin gada a sassan birnin Kano domin samar musu da kyakkyawar makoma da kuma maslahar al’umma.

“Yaran da za mu fara kamawa sune waɗanda suke kamar an zubar da su yawo kan titi, waɗanda ba su da wata makoma, mafi yawansu ba a san daga inda suke ba. Waɗansu ‘yan Kano ne wasu yan wasu jihohin wasu kuma ‘yan wajen ƙasar nan ne ma,” in ji Ɗaurawa

“Wasunsu rayuwa ce ta yi musu tsauri ta gagara suka koma kwana ƙarƙashin gada da gareji da wajen tuburan masu shayi. Irin waɗannan yaran mai girma gwamna ke fatan a kama a tantance na gida da na wajen a san matakin da za a ɗauka a kansu.

“A basu tarbiyya a mayar da su cikin al’umma domin su zama masu amfani ka da su zama barazana ga al’umma,” in ji Malam Aminu Daurawa.

Wannan kwamitin dai ya ƙunshi wasu ƙananan kwamitoci waɗanda za su yi aikin tantance yaran ta fuskar lafiya da sauran bayanai.

Sheik Daurawa ya ce ba za a faɗi yaushe za a fara wannan aiki ba domin ka da waɗanda ake son a taimakawa su tsere a gaza cimma manufar aikin.

“An bamu filin sansanin alhazai da ke kusa da filin jirgin sama, a nan za mu ajiye su tsawon makonni biyu mu tantance su da lafiyarsu da kuma garuruwansu.

“Za a yi aikin nan ne ƙarƙashin kwamiti guda huɗu da za su kammala aikinsu cikin kwana 14 sannan gwamna ya bayyana mataki na gaba,” in ji Malam Aminu Daurawa.

To sai dai ‘yan kungiyoyin da ake aikin kare kananan yara na ganin akwai bukatar gwamnati ta lura da wasu mahimman abubuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp