Home General Najeriya ta roƙi Chadi kada ta janye daga rundunar ƙasashe ta yaƙi...

Najeriya ta roƙi Chadi kada ta janye daga rundunar ƙasashe ta yaƙi da Boko Haram

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya tura wata tawaga mai ƙarfin gaske zuwa N’Djamena, babban birnin Chadi bayan da Shugaban Chadin ya yi barazanar janye dakarun ƙasarsa daga rundunar haɗaka ta yaƙi da ‘yanta’adda a yankin Sahel.

A jiya Lahadi ne tawagar ta Najeriya ta je N’Djamena, inda a can hedikwatar rundunar (MNJTF), da ta ƙunshi dakarun Najeriya da Nijar da Chadi da Kamaru da Jamhuriyar Benin, take.

Shugaba Deby ya yi barazanar janye sojojin ƙasarsa ne bayan da mayaƙan da ake zargi na ƙungiyar Boko Haram ne suka kashe dakarun ƙasarsa 40 a tsibirin Barkaram, da ke yankin tafkin Chadi a ranar 27 ga watan Oktoba.

Saboda wannan barazana ne shugaban na Najeriya ya tura tawagar ƙarƙashin jagorancin mai ba shi shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, domin tattauna batun haɗin kan tsaron.

Rahotanni sun ce, bayan gabatar da ta’aziyyar Shugaba Tinubu ga Shugaban na Chadi kan rasa sojojin, tawagar ta tabbatar wa da shugaban na Chadi samun cikakken goyon bayan Najeriya wajen yaƙi da ta’addanci.

Babban hafsan hafsoshin Najeriya Janar Christopher Musa, wanda shi ma yake cikin tawagar ya ce ƙudurin sojin ƙasashen biyu zai tabatar da nasarar yaƙi da ‘yanta’adda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp