Home General Mutum uku ke magana da yawuna – Tinubu

Mutum uku ke magana da yawuna – Tinubu

Fadar shugaban Najeriya ta ce shugaba Tinubu ya yi garambawul game da ayyukan jami’ansa da ya naɗa a sashen hulɗa da kafafen yaɗa labaru, domin bunƙasa ɓangaren.

Wata sanarwa da mai taimaka wa shugaba Tinubu kan yaɗa labaru da tsare-tsare, Bayo Onanuga ya fitar ta ce a yanzu dukkanin mutane uku da aka naɗa a muƙaman yaɗa labaru za su zamo masu magana da yawun shugaban ƙasa.

Sai dai sanarwar ta ce Mista Sunday Dare a yanzu shi ne mai bai wa shugaban ƙasar shawara na musamman kan kafafen yaɗa labaru da hulɗa da jama’a.

Haka nan Mista Daniel Bwala, wanda a makon da ya gabata aka bayyana a matsayin mai bai wa shugaban ƙasa shawara na musamman kan kafafaen yaɗa labaru da sadarwa yanzu zai riƙe muƙamin mai bayar da shawara na musamman kan yaɗa manufofin gwamnati.

Sanarwar ta ce idan aka yi la’akari da cewa akwai kuma Bayo Onanuga, wanda shi ne mai taimaka wa shugaba Tinubu kan yaɗa dabarun gwamnati “za a ga cewa babu mutum ɗaya tilo da ke riƙe da muƙamin mai magana da yawun shugaban ƙasa”.

“Saboda haka dukkanin mashawartan na musamman uku za su zamo masu magana da yawun gwamnati.”

An dade dai ana raɗe-radin cewa akwai rashin jituwa a ɓangaren masu taimaka wa shugaba Tinubu kan yaɗa labaru, inda ayyukan wasu jami’an ke shiga cikin na wasu.

A cikin watan Satumban da ya gabata ne, mai magana da yawun shugaban ƙasar, Ajuri Nagelale ya ajiye muƙaminsa ‘bisa wasu dalilai na ƙashin kai’ kamar yadda ya bayyana.

Sai dai kafafen yaɗa labaru da dama sun yi bayanin cewa ajiye muƙamin nasa ba zai rasa nasaba da rashin jituwar da ke tsakanin jami’an da shugaba Tinubu ya naɗa a ɓangaren yaɗa labarun na fadar shugaban ƙasa ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp