Home General Jihohi biyu ne kaɗai za su amfana da sabuwar dokar harajin Najeriya...

Jihohi biyu ne kaɗai za su amfana da sabuwar dokar harajin Najeriya – Zulum

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya bayyana dalilin da ya sa gwamnonin Arewa suka shawarci shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya ɗan dakata kafin ya tura daftarin dokar sake fasalin harajin ƙasar zuwa majalisar dokoki.

Gwamnan wanda ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da gidan Talabijin na Channels ranar Lahadin da ta gabata, ya ce ƙungiyar gwamnonin Arewa na buƙatar lokaci ne domin tuntuɓa da kuma nazarin ɓangarorin dokar harajin.

“A kan wannan dokar, akwai abubuwa da dama da ba a fahimta ba. Mun duba tanadin da aka yi wa harajin VAT a cikin dokar. Bisa kididdigar da muka yi, Jihohin Legas da Ribas ne kaɗai za su ci gajiyar waɗannan sauye-sauyen. Mun yi namu binciken kuma mun gano cewa za mu yi asara,” inji Zulum.

“Me yasa muke hanzari? Mun shawarci Gwamnatin Tarayya da ta dakata, ta yi kakkaɓe wasu abubuwan da za su iya cutar da yankin Arewacin Najeriya.”

Zulum ya yi bayanin cewa idan har dokar ta sami amincewar Majalisar Dokoki ta kasa, za a cutar da jihohi da dama domin jihar Legas ce kaɗai za ta ci gajiyar wannan manufa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp