Home General Majalisar Dattijai Ta amince da dokar haramta fitar da Masara daga Nijeriya

Majalisar Dattijai Ta amince da dokar haramta fitar da Masara daga Nijeriya

Majalisar DattawaN Nigeriya ta amince da gyaran dokar da ta haramta fitar da tsabar masara (wadda ba a sarrafa ba), inda ta tanadi hukuncin ɗaurin shekara guda ga waɗanda suka karya wannan doka.

Dokar, wadda ta samo asali daga Majalisar Wakilai, tana nufin hana fitar da masara mai yawa, musamman wadda ta kai ko ta haura ton ɗaya.

Ta kuma tanadi tara mai tsada daidai da kimar kayan da aka fitar ko ɗaurin shekara guda ko kuma haɗa hukuncin biyu ga waɗanda suka keta wannan doka.

Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele na jam’iyyar APC dake wakiltar alúmmar Ekiti ta tsakiya, yayin gabatar da dokar, ya bayyana muhimmancinta wajen magance matsalar ƙarancin abinci a Najeriya.

“Wannan doka mai sauƙi ce kuma an bi dukkan matakan doka da suka dace wajen nazarinta. Ina roƙon abokan aikina su goyi bayanta,” in ji shi.

Sanata Garba Maidoki (PDP, Kebbi South) ya gabatar da gyara don cire abubuwan da ake sarrafawa daga masara, kamar garin masara da man ganye, domin kare amfanin manoma da masana’antun cikin gida.

Gyaran ya sami amincewa bayan ƙuri’ar jin ra’ayin bakunan ‘yan majalisar.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, wanda ya jagoranci zaman, ya ce barin abubuwan da ake sarrafawa daga masara zai taimaka wajen ƙirƙirar ayyukan yi.

“Waɗannan abubuwan suna da matuƙar muhimmanci wajen samar da ayyukan yi. Cire su ya dace da manufofin tattalin arziƙinmu,” in ji Jibrin.

Dokar da aka gyara za ta ci gaba zuwa kwamitin sulhu don daidaita bambance-bambance tsakanin Majalisar Dattawa da ta Wakilai kafin a miƙa ta ga shugaban ƙasa don rattaba hannu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp