Home General Majalisar Dattijai Ta amince da dokar haramta fitar da Masara daga Nijeriya

Majalisar Dattijai Ta amince da dokar haramta fitar da Masara daga Nijeriya

Majalisar DattawaN Nigeriya ta amince da gyaran dokar da ta haramta fitar da tsabar masara (wadda ba a sarrafa ba), inda ta tanadi hukuncin ɗaurin shekara guda ga waɗanda suka karya wannan doka.

Dokar, wadda ta samo asali daga Majalisar Wakilai, tana nufin hana fitar da masara mai yawa, musamman wadda ta kai ko ta haura ton ɗaya.

Ta kuma tanadi tara mai tsada daidai da kimar kayan da aka fitar ko ɗaurin shekara guda ko kuma haɗa hukuncin biyu ga waɗanda suka keta wannan doka.

Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele na jam’iyyar APC dake wakiltar alúmmar Ekiti ta tsakiya, yayin gabatar da dokar, ya bayyana muhimmancinta wajen magance matsalar ƙarancin abinci a Najeriya.

“Wannan doka mai sauƙi ce kuma an bi dukkan matakan doka da suka dace wajen nazarinta. Ina roƙon abokan aikina su goyi bayanta,” in ji shi.

Sanata Garba Maidoki (PDP, Kebbi South) ya gabatar da gyara don cire abubuwan da ake sarrafawa daga masara, kamar garin masara da man ganye, domin kare amfanin manoma da masana’antun cikin gida.

Gyaran ya sami amincewa bayan ƙuri’ar jin ra’ayin bakunan ‘yan majalisar.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, wanda ya jagoranci zaman, ya ce barin abubuwan da ake sarrafawa daga masara zai taimaka wajen ƙirƙirar ayyukan yi.

“Waɗannan abubuwan suna da matuƙar muhimmanci wajen samar da ayyukan yi. Cire su ya dace da manufofin tattalin arziƙinmu,” in ji Jibrin.

Dokar da aka gyara za ta ci gaba zuwa kwamitin sulhu don daidaita bambance-bambance tsakanin Majalisar Dattawa da ta Wakilai kafin a miƙa ta ga shugaban ƙasa don rattaba hannu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp