Home General Sojoji kaɗai ba za su iya samar da tsaro a ƙasa ba...

Sojoji kaɗai ba za su iya samar da tsaro a ƙasa ba – Janar Chris Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya ce karfin soji kaɗai ba zai samar da tsaron da ake buƙata ba a Najeriya.

Ya ce amfani da karfin soji na bayar da gudummawar kashi 30 cikin ɗari ne kacal na tsaron ƙasa, yayin da kashi 70 ya dogara kan siyasa da kuma tallafi ga walwala da na tattalin arzikin al’umma.

Janar Musa ya bayyana haka ne a wani taro kan tsaron ƙasa da cibiyar daƙile ayyukan ta’addanci karkashin ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkar tsaro ya shirya a Abuja.

Babban hafsan ya buƙaci haɗin gwiwa wajen daƙile matsalar rashin tsaro a Najeriya.

“Dole ne a haɗa karfi da karfe wajen magance matsalar tsaro, musamman ganin rikice-rikice da kuma rashin tabbas da ya dabaibaye mutane,” in ji shi.

Ya ce mutane sun ɗauka cewa sojoji ne kaɗai za su samar da tsaro ba tare da la’akari kan irin gudummawar da kowane ɓangare zai bayar ba wajen tabbatuwar hakan.

Ya ƙara da cewa ƴan jarida ma na da rawar da za su taka wajen tabbatar da tsaro a faɗin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp