Home General Sanatocin yankin Igbo sun nemi a sake duba ƙudurin haraji na Tinubu

Sanatocin yankin Igbo sun nemi a sake duba ƙudurin haraji na Tinubu

Sanatocin yankin kudu maso gabas sun shiga sahun waɗanda suke kira da a sake duba ƙudurorin haraji da shugaba Tinubu ya aika majalisa.

Jagoran gamayyar santocin yankin, Sanata Enyinnaya Abaribe (ɗan jam’iyyar APGA, mai wakiltar Abia ta kudu) ne bayyana hakan ga manema labarai bayan taron sanatocin daga jihohi biyar na yankin kudu maso gabas a ofishinsa.

Abaribe ya ce sanatocin yankin ba suna cewa a yi watsi da ƙudurorin ba ne, suna so a faɗaɗa tattaunawa, sannan a samu ƙarin lokaci domin su samu damar ganawa da waɗanda suke wakilta da sauran masu ruwa da tsaki kafin a ɗauki wani mataki a game da ƙudurorin.

Ya ƙara da cewa, “mun yi nazarin ƙudurorin sosai, sannan mun yanke shawarar cewa akwai buƙatar mu ƙara tattaunawa da dukkan masu ruwa da tsaki daga yankin kudu maso gabas. Muna so yi hakan ne domin tabbatar da cewa ƙudurorin sun yi amfani ga ƴan Najeriya, musamman yankinmu,” in ji Abaribe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp