Home General Sanatocin yankin Igbo sun nemi a sake duba ƙudurin haraji na Tinubu

Sanatocin yankin Igbo sun nemi a sake duba ƙudurin haraji na Tinubu

Sanatocin yankin kudu maso gabas sun shiga sahun waɗanda suke kira da a sake duba ƙudurorin haraji da shugaba Tinubu ya aika majalisa.

Jagoran gamayyar santocin yankin, Sanata Enyinnaya Abaribe (ɗan jam’iyyar APGA, mai wakiltar Abia ta kudu) ne bayyana hakan ga manema labarai bayan taron sanatocin daga jihohi biyar na yankin kudu maso gabas a ofishinsa.

Abaribe ya ce sanatocin yankin ba suna cewa a yi watsi da ƙudurorin ba ne, suna so a faɗaɗa tattaunawa, sannan a samu ƙarin lokaci domin su samu damar ganawa da waɗanda suke wakilta da sauran masu ruwa da tsaki kafin a ɗauki wani mataki a game da ƙudurorin.

Ya ƙara da cewa, “mun yi nazarin ƙudurorin sosai, sannan mun yanke shawarar cewa akwai buƙatar mu ƙara tattaunawa da dukkan masu ruwa da tsaki daga yankin kudu maso gabas. Muna so yi hakan ne domin tabbatar da cewa ƙudurorin sun yi amfani ga ƴan Najeriya, musamman yankinmu,” in ji Abaribe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp