Home General Sanatocin yankin Igbo sun nemi a sake duba ƙudurin haraji na Tinubu

Sanatocin yankin Igbo sun nemi a sake duba ƙudurin haraji na Tinubu

Sanatocin yankin kudu maso gabas sun shiga sahun waɗanda suke kira da a sake duba ƙudurorin haraji da shugaba Tinubu ya aika majalisa.

Jagoran gamayyar santocin yankin, Sanata Enyinnaya Abaribe (ɗan jam’iyyar APGA, mai wakiltar Abia ta kudu) ne bayyana hakan ga manema labarai bayan taron sanatocin daga jihohi biyar na yankin kudu maso gabas a ofishinsa.

Abaribe ya ce sanatocin yankin ba suna cewa a yi watsi da ƙudurorin ba ne, suna so a faɗaɗa tattaunawa, sannan a samu ƙarin lokaci domin su samu damar ganawa da waɗanda suke wakilta da sauran masu ruwa da tsaki kafin a ɗauki wani mataki a game da ƙudurorin.

Ya ƙara da cewa, “mun yi nazarin ƙudurorin sosai, sannan mun yanke shawarar cewa akwai buƙatar mu ƙara tattaunawa da dukkan masu ruwa da tsaki daga yankin kudu maso gabas. Muna so yi hakan ne domin tabbatar da cewa ƙudurorin sun yi amfani ga ƴan Najeriya, musamman yankinmu,” in ji Abaribe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp