Home General Sabon shugaban ƙaramar hukumar Gwale, Mojo, ya yi barazanar sauka daga kujerarsa

Sabon shugaban ƙaramar hukumar Gwale, Mojo, ya yi barazanar sauka daga kujerarsa

Shugaban Ƙaramar Hukumar Gwale, Abubakar Muazu Mojo ya yi barazanar ajiye aikinsa na shugabancin karamar hukumar muddin ba’a sauya masa Daraktan Mulki, DPM, na karamar hukumar ba.
jaridar DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa tuni dai Shugaban karamar hukumar ta Gwale ya bada umarnin a rufe ofishin DPM din, Danjuma Zubairu Bebeji.
A wani sakon murya da Mojo ya aikewa manema labarai, ya yi ikirarin cewa idan har Daraktan Mulkin bai bar karamar hukumar ba to shi zai bar masa wajen.
Ya kara dacewa manufofin Daraktan Mulkin sun saɓa da tsarin Kwankwasiyya na yi wa jama’a hidima da taimako.
Rahotanni sun baiyana cewa Mojo da DPM ɗin sun jima su na takun saƙa tun lokacin da ya ke Shugaban riko na karamar hukumar ta Gwale kafin a zabe shi a watan Oktoba.
Daga cikin zarge-zargen da Mojo ke yi wa Bebeji har da yi wa karamar hukumar zagon kasa da hana tafiyar da aiki yadda ya kamata, gami da sakaci a wajen aikinsa da hakan ya janyo wasu mahimman takardu su ka ɓata.
Saboda haka ne shugaban karamar hukumar ya ce idan ba a ɗauke Bebeji ba, to shi da majalisar kansilolin sa za su sauka su bar masa wajen.
Sai dai kuma har yanzu ba a ji ta bakin DPM ɗin ba.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp